Ramadan Kareem

An ga watan azumin Ramadan a Najeriya 2023…

Sponsored Links


 Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar na uku ya sanar da ganin jaririn watan Ramadan na shekarar 2023 a wasu sassan Najeriya.

A jawabin da ya yi na sanarwar wanda aka sanya a shafin Tuwita na kwamitin ganin watan, Sarkin Musulmin ya ce an ga watan ne bayan samun rahotanni daga shugabannin addinin Musulunci da ke wasu jihohin ƙasar.

Hakan na nufin ranar Alhamis 23 ga watan Maris din 2023 ne za ta kasance daya ga watan Ramadan.

Leave a Reply

Back to top button