Hausa NovelsHausa NovelsZafin Kai Hausa Novel

Zafin Kai 24

Sponsored Links

24

A motarsu ta dawowa tinda suka shigo hande Ce Mai magana cikin takacinsu Dana uwarsu sai fada takeyi tana qarawa Amma Babu Mai iya ko dogon motsi a cikinsu bare dagowa su tanka,

Hankalinsu da tashin hankalinsu Yana kan Ababa ne da yake shiru har lokacin Bai Ce qala ba,

Idanuwansa sun kada sinyi jajir sbd tafasar zuciya da bacin ran dayake fal cikinsa.

Suna isowa nesa da gida aka ajiyesu ya biya Mai taxi suka nufi hanyar gida.

Duk taku daya dasu benazir keyi na hanyar zuwa gidan bugun zuciyarsu da numfashinsu sauyawa yakeyi har suka iso.

Annensu da tin bayan fitarsu kowane second daya shude fargabarta da tsoranta qaruwa yakeyi,

Aikin girkin da aka barta tai na Rana har suka je suka dawo Bata iya aikata komaiba sbd Bata cikakken hayyacinta matiqar ba yayanta taga sun dawo mata ba,

Tsoro da tashin hankalin datake ciki Mai girma ne sbd tinaninta da sanin Ababa zai iya Kai mata yayan wani guri ya barosu akan wannan laifin dasuka aikata.

Suna shigowa ta miqe tsaye daga zaunen datake tsakar gida tana jiran tsammani,

Idanuwanta akan Yayanta suke saidai kafin tai yunqurin Isa garesu Ababa ya dago fuskarsa yana zama kan kujerar robar zamansa Dake tsakar gidan.

Numfashi ya sauke tsawon mintina kafin ya dago ya kallesu daya bayan daya ya zare hular Kansa ya ajiye gefe tareda nade hannuwan rigarda daga zaunen cikin kwantar da hankali yace

“Wannan cikin zaa min bayaninsa Dalla Dalla,

yaushe aka samesa,

Dan gidan uban waye yayisa kokuma uban waye yayisa,

Tayaya aka Sami wannan damar,

Yaushe kuka San dashi aka boye min Kuma ubanwaye a cikinku ya Bada shawarar a boyemin,

Komai Zaku fada mun daya bayan daya kafin yanzu ta haife shege Dan bazai kwana a cikinta yau dinnan ba.

Sumayyah ya kalla wadda tini qafafunta suka fara mazari suna Neman gagara tsayuwa.

Kan benazir da itama take rawar jikin ya maida idanuwansa kafin daga qarshe ya jefawa Anne nata kallon Yana tinanin ita yanda zaiyi da ita idan ya gama da wainda ta daurewa gindi akaci Amanarsa a cikin gidansa.

Shirunsu yasa zuciyarsa qarasa birkicewa a haukace yayi ball da butar hande Dake kusa Yana cewa Zaku min bayanin ko saina taka wuyan uwarku gatanan.

Rawa jikin sumayyahn ya dauka take ta rude harshenta ya karye takasa magana ta zube qasa kan gwiwowinta tana Neman hawaye daga idanuwanta da Sukai jajir din tashin hankali.

Wuyanta ya kamo ya sauke mata wani lafiyayyan Marin daya sata qarasa rudewa tana kasa magana ga wuyanta a hannunsa Yana neman rabata da numfashinta.

Cikin zafi ya sake shaqar wuyan nata Yana cewa

“Ubanwaye yayi Miki cikin?

Ni Zaku yaudara?

Ni Zaku ciwa mutunci?

Ni Zaku tozarta?

Yaushe kuka Sami damar da har kuka fara Kula Wanda yayi Miki cikin??

Firfitowa idanuwanta sukai tana shura qafa azaba zatasa ta rasa ranta…

Cikin tashina hankali da tsoro Mai tsananin gaske benazir tace

“A makaranta suka hadu ya taimaka ya kaimu asibiti batada lfy,

Sunansa ALH BILAL KAANTE.

Shiru yayi tareda juyowa ya kallo Benazir da jajayen idanuwansa sbd kunnuwansa da kaman Basu Ji masa daidai ba,

Shirun minti daya yayi Yana neman Inda zai Dora zacenta cikin Kansa Amma ina Sam zancen Bai doru ba Dan haka ya sake danqar wuyan sumayyahn Yana cewa gwara ta mutu data haifar masa wannan cikin wlh.

Cikin kuka mara sauti da tashin hankali da tsoran karya kashe sumayyahn ta sake cewa

“Wallahi Ababa sunansa Alh Bilal kaante,

Shine…shine hakan ta faru dashi…

Sakin sumayyahn yayi ya fizgo Benazir din cikin zafi da wutar Dake cin Kansa Ya daga hannu zai mareta sbd Kansa ya kasa dauka zancen nata Neman cinna masa hauka takeyi yanajin kaman tana fadan sunan Alh Bilal kaante a matsayin uban cikin,

KAANTEs KAANTEs dai daya sani a labarai da jarida take fada,

Ta Ina?

Ta Yaya?

Gari Yaya?

Cikin azaba murya Bata fita daqyar sumayyah ta Bude Baki tace

“Shine,

Bilal kaante…

Dauke wuta Ababan yayi Yana juyowa ya kalli sumayyahn sbd yanda ta fadi sunan Bilal din zalla ba Alhaji ba sir da alaman da gasken kenan,

Amma tayaya kansa zai dauki wanna zancen?

Tayaya zasu Ce masa cikin nan Dan kaantes ne yayi sa.

Inaaaa haukatasa zasuyi wlh dukan rini zai musu su dawo hayyacinsu idanma ciwon qwaqwalwa ya kamasa su dukan.

Janyosu yayi ya hade guri daya ya fara duka Anne tayi saurin zuwa ta zube gabansa cikin magiya da kaskantar da Kai tahau rantsuwa akan Bilal dinne.

Bai saurara Saida Benazir ta sake rantse masa da Allah cikin azaba da wahala sbd kusan dukan kare sumayyah taita Yi Yana sauka kanta sbd cikin.

Hande data rasa gane kan zancen cikin zafi ta taresa ta janye gefe tana cewa

“Ba gashi sun fada sunan me barnar ba meyasa bazaka tsaya kaji sauran bayaninba asan hanyar bi.”

Kallan hande yayi zaiyi magana sai ya fasa sbd bazata fahimci mema zai fada din ba Dan haka ya juya a zafafe yabar gurin ya fada dakinsa sbd bacin ransa da baqin cikinsa ayau Babu wanda yakaisa shi a Dunia.

Cikin sauri da tausayi Anne tayi kan Yayanta ta kamasu suka miqe tayi daki dasu.

Zaunar dasu tai Allah yasa Basu wani daku ba Dan haka itace yau tayi musu gashin jikin suka Dan Ji sauki tafito ta Dora abincin Rana kafin ya nema ace batayiba.

Hankalinta a rarrabe tayi aikin tagama lokacin har sunyi sallar azahar,

Sumayyah Ce kejin zazzabi Amma benazir dole ta warware sbd kada aikin yawa Annen yawa.

Shiru gidan yayi har yamma Babu motsin kowa Suma suna daki sbd dukkaninsu Ba Wanda bejin zazzabi Amma sumayyah Ce kawai ta Sami damar kwatawa sbd yafi mata karfi akansu sbd yanayinta.

Haka suka wuni cikin zullumi da wasi wasi tareda fargaba har dare yayi har sika kwanta Ababa Bai sake nemansu ba.

Yau dayake tana Jin zazzabi fiye da jiyan duk yanda taso gadinsu kada a riskesu da daddare a illata su bacci Bai barta ba 12 na yi bacci Mai karfi ya dauketa itama jiki duk a mace.

Washe gari qarfe 7 na safe Ababa yasake Kiran kowa qaramin palonsa suka zazzzauna Yace yanzu Yana sauraro ai masa bayanin ta Yanda sukasan Alh Bilal kaante din har ake maganar shine uban cikin.

Wanna Karan sunsan suba tsimi ba dabara Dan haka jiki mace a tsorace sumayyah na rawar jiki Harma data harshe ta fada masa a makaranta suka hadu ya ringa bibiyanta akan Yana sonta.

Daga Nan shiru tayi sbd batasan me zata fada ba Dan bazata iya fadan abubuwan daya ringa ciyar dasu ba da yanda suke shiga motarsa da napep daya siya don kaisu makaranta Harma da yanda yaje da ita gidan qaninsa kaddarar samun cikin ta samesu.

Idan ta fada wannan bayanin kashesu zaiyi take a gurin shiyasa rudewarta ma Bata kaita fada ba.

Shiru yai Shima sbd har lokacin ya kasa gamsuwa da zancen shigowar Alh Bilal kaante cikin zancen cikin nan,

To Amma shi mutum ne Mai komai akan lissafinsa da tsarinsa daya San zai fiddasa

Dan haka ya kwana Yana nazari da lissafi da tinani daban daban.

Idan har Alh Bilal kaante ne uban cikin ba maganar haihuwar ciki yanzu sai ya girma ya Isa haihuwa sbd lissafi da zance ya canja gabaki daya,

Yanzu kam wani labarin zasu Dora ba na baya ba,haduwarsa da Alh Dd babba kaante yazo.

Amma bazai Yi garaje ba sai ya tabbatarda gaskiar maganarsu tukuna.

Kallan Anne yai cikin takacinsu Yana Jin kaman ya mangareta Yace

“Kiyi adduar ‘yayanki ba qarya suka fadamun ba Dan kuwa Idan nagama gano qarya suka fadamun Dan na barsu wlh cikinku ba tsira Zaku ga asalin fushi Wanda Baku taba gani ba”

Kan benazir ya maida kallansa Yace

“Ke Kuma naga alaman Nemo muku hanyar rabuwa da cikin kikeyi wlh motsi daya ban yarda ayisa a gidan Nan ba tareda sanina ba,

Har cikin yanzu ban yarda da wani motsi akansa ba Bada izininaba,

Tinda ta dauko cikin masu karfi wlh saita haifesa da izinin Allah Daman can Banda niyar zubar mata da cikin haifesa naso tayi yanzu lokaci ne na qara mata maimakon haihuwar yau din.

Hande ya kalla Yana sake matse fuska Yace

“Ki Saka ido Sosai kan yaran Nan sbd Tim farko kece kikai sake duk wannan ya faru,

Gashi yanzu Kuna nema zautani da tinani da lissafi,

Wlh na zaune a gidan Nan kowama yasan mokamarsa”.

Yacewa yayi kowa ya fice yabasa guri.

Kaman munafukai haka suka fito daya bayan daya suka koma dakinsu saidai ko zama Basuyi ba hande ta Kira Benazir ta fito aiki.

Sumayyah yanzu da aka San da cikin hakanan dole ta fito Dan kamawa benazir din aiki da Anne.

Ba Bata lokaci suka gama dafa Karin safiyar,taliya Ce da Alayyahu.

Ana Basu nasu suka ci sbd Basu taba tinanin abun zaizo da sauki haka ba,

Babu Wanda Bai sadaqar da barin Dunia ba acikinsu Amma sai gashi Ababan yazo da sauki Amma dai duk da hakan basu cire ran masifar na kwance tana jiransu bane.

Anne kuwa tashin hankalin Dake cin ranta da tsananin damuwa da fargabarta kada Ababa ya nemi Alh Bilal din Yace baisan da cikin ba,

Idan haka ta faru tabbas ‘yarta na cikin mawuyacin Hali Dan su Basu damu da duk abinda zai musu ba kaman abinda zaiwa sumayyahn,

Ita benazir Bata shiga shakka da tsoran abinda Alh Bilal zai fada ba sbd ta shedar da tsananin son dayakewa sumayyah bazai gujetaba Amma dai ta yanda Ababan zai tinkaresa da yanda lamarin zai kasance ne tsoronta da tashin hankalinta.

Sumayyah kuwa a yanzu jikinta yayi sanyin da batada saura tinani ko fargaba,

Qaddara dai ta Riga ta hau kanta,

Batada ikon kanta batada dabarar kanta,

Idan aka barta ta haifesa da acire mata shi duk batada tacewa ko zabi sbd kowanne Akai mata rayuwarta ta Riga ta lalace.

****Kwana biyu Ababa Bai sake tada maganar cikin ba ya kyale kowa sbd tsananta bincikensa dayakeyi ba dare ba Rana akan Familyn kaantes,

A saninsa dukiyarsu a bayyane take gurin alumma Amma daya tsananta bincike sai gashi Yana Jin dukiyoyin Dake Neman juyar da lissafinsa,

Komai nasa a tsarin lissafi yake binsa shiyasa yake wani mugun bincike akansu na boye dayake buqatan sanin duk wani sirrinsu na Fili Dana boye sbd Yana tinkararsu da maganar cikin ‘yarsa zancen ma a masa musu Bai taso ba asiri rufe a karba cikin.

#MAMUH#

#DD KAANTE

#BENAZIR ABABA

#AMNAH KAANTE

#CRAXYinlove

#contract

#ZAFIN KAI

25

*_Arewabooks@Mamuhgee_*

Leave a Reply

Back to top button