Hausa NovelsTUMFAFIYA Complete Hausa Novel

TUMFAFIYA 24

Sponsored Links

 

,,,,,,,

 

 

Wanan labarin na sayar dashi don alredy don haka kada wani
yai kasadan juya min shi zuwa audiovisual yin hakan gangancine ga maishi.

  Dari biyar ne ki
biya don Allah ki karanta a cikin sallama yar uwa don Allah ki biya ki gujewa
daukan alhaki a kanki yar uwa.

    Kuka nakeyi sosai
kamar raina zai fita din maganganun da yake fada min masu tayar da hankali yana
kuma kara kashe min jiki da kalaman shi da sunan ban hakkuri a garemu.

   Kunnuwana ba zasu
iya daukan kalaman shi tun lokacin daya furta zarah dole hakkuri zamuyi da juna
don gudun birewa iyayyen ki a kaina dan zaman mu tare zai iya jawo maki matsala
da rayuwaka zasu baci.

   Don gaskiya Abba ya
fadi ni daya nake da maraya ko wani mara uba dayazo duniya don haka kinga banda
asalin da zamu iya zama a tare dake har iyayyenki suyi suyi alfahari da hakan
don tabon da iyayyena suka shafawa rayuwata.

  Dif na kashe wayan
saboda cigaba da saurarenshi zai iyasa zuciyana bugawa a lokacin don yadda nake
jin kaina haka shima baiyi gigin sake kiran layin nawa ba a lokacin don kukan
da yazo mashi.

   Kuka yake saboda
abu biyu na farko gorin da yasan zan biyo bayanshi dama ako gidanwa yaje neman
aure balle irin gidan mu babban gida irin haka da kaddara takaishi ciki.

    Shi kanshi yasan
duk wanda yaji hakan ba za,a taba bashi gaskiyan hakan daya faru ba don ko
driver ya samu a gidan mu yaci a kalleshi a daga mashi hannu.

   Balle wai aji yar
gidan mune yake nema da aure a lokacin idan ba kaddara ba waya isa yai hakan
saiko kaddara din da yanzu aka fake a gareta.

    Ya dade a kwance
yana kuka shi kadai a dakin kukan nasa yasha bambam danawa domin shi kukan abu
biyu yakeyi a lokacin niko ina kukane kan kalaman Abba garemu kadai.

   Yayin da shi kuma
yake kuka kan irin rayuwan da mahaifan shi suka sakashi cikine don abin fade
baiwa mutune kadan yanzu koda abin na a taru a tausayawa mutum ne sai an koma
baya ayin gulman mutum a karshe.

    Yasan kulba dade
dama zai samu irin hakan saidai bai taba tsamanin hakan da wuri ba gareshi sai
gashi ya fara fuskantan hakan ga babban mutum kamar Abban mu daya nuna mai
kyama ko tsana kan kawai don matsala irin ta iyayyenshi dake binne shekara da
shekaru.

     Motsinshi da Dije
taji na fitowanshi daga dakin ya nufi bandakin yasa ta fitowa tana fadin Amadi
kana gidan nan dama ashe ?

    Eh kawai ya amsa
mata ba tare daya tsaya ba a cikin dakusheshen muryan shi da kuka yasashi
narkewa hakan lokaci guda.

    Kallon mamaki da
zargin ko baida lafiyane ta tsaya take mashi lokaci guda tana tsaye har ya fito
ya tsuguna daga can ya samu wuri ya fara alwala a gurguje.

   Ya gama ya mike
tana fadin abincin ka na nan tun dazun a daki me yuyuwa ma yanzu yayi sanyi don
tunda sauran rana nayishi barshi Dije yau banjin yunwa ya fada yana wucewa ba
tare daya dan tsaya magana da itaba yadda suka saba idan ya ganta tsaye.

   Ya shige dakin shi
ya fara sallah komawa Dije tayi dakinta cike da zarginshi a zuciyar ta can taji
ya rufo kofan gidan su kafin taji yana rufo kofan dakin nasa kuma haka yasa ta
mike ta fito har zuwa kofan shi tana fadin.

   Amadi haka zaka
kwanta ba tare da kaci wani abu a cikinka ba ka kwana hakana da yunwa ka fito
ko shayi ka fita ka samo kasha son babu ruwan zafi a gidan nan yanzu.

     Dije bana iya cin
komai jeki kwanta kawai dare yayi yanzu karfe tara saura zakace darene yanzu
meke damun kane yau din nan wai ?

   Dije ta tambaya
daga waje duk da yaji muryanta hakan
baisa ya bude kofanba bai kuma bata amsa ba yayi shiru kamar bai cikin
dakin a lokacin.

    Munaga rasul Dije
ta fada ta juya tana cigaba da fadin yaron nan kanshi daya kuwa yau din nan
yaro haka kamar wanda yai gamo a hanya Allah ka cecemu ta fada ta koma dakinta.

   Gidan yai shiru
kowa na part din shi tare da yaran shi don ni tun safe ban leko waje ba ina
dakina kwance hjy tsohuwa ce ta shigo tare da wasu jikokinta mata biyu da suka
rakota.

   A ka,ida dakin
ummah takan fara shiga kafin ta koma dakin mama ta zauna har zuwa lokacin da
zata bar gidan idan tazo gidan mu.

   Saidai hakan bai
hana ummah hidima da zuwan nata zata girka mata abinci koda batayi niyar yin
girki na musanman ba a ranan zatayi hidima sosai wa hjyn akai mata can falon
mama inda zasu zube kowa yaci yasha wani lokacin ma bata sanin tafiyan su
saidai taji cewa sun wuce.

    Ta shigo bata ko
zauna bata ko zauna ba a ranan a tsatsaye suka gaisa da ummah din ta juya ta
fita zuwa dakin hjy karima tunda yanzu sun zama su uku a gidan .

   A can ma din bata
tsaya ba ta fito ta zarce dakin hjy mama a can suka zauna kowa yaci gaba da
harkokin shi a part dinshi sai zuwa ranane mama ta aiko wai idan ummah ta gama
abinci a kawo wa hjy.

    Ummah tace abinci
yau banyi girki ba don yaran ma basu zauna ba basu gida komai ban girkaba a
part din nan saida yamma zanyi abinci.

  Ai ana fadi mama
tace zancen banza ke nan ki koma kice mata bata sanda cewa a nan hjy zata wuni
bane bata girka mata abinci ba.

   Yarinyar ta dawo ta
fadawa ummah sakon mama tace jeki kicewa maimuna nace ko ta manta itace da
girki yau ne ?

    Nan mama ta
harzuka wai ita ummah zata aikowa maganan banza har ta aiko mata da wani zancen
haka ita ummah ta aika mata da zancen zafi.

   Har yakai hjy din
ta mike wai zata tafi gida tunda ba a san darajanta ba a gidan Abba din dama
inda mama keson akai ke nan Aisha ce ta samu Abba a fslon shi hankali tashe
take fada mai abinda ke faruwa a cikin gidan namu.

    Mamaki sosai Abba
yayi da jin hakan a take ya tarasu a falon shi ranshi bace yake sosai jin cewa
wai unmade taki girjawa hjy abinci ga kuma fitina da ya biyo baya.

   Har hjy din duk
suna falo da matanshi ukun suna shigowa daya bayan daya kusan ummah ce ta shigo
a karshe yanayinta kawai zaka kalla kasan bata jin dadin jikinta ko tana cikin
damuwa a lokacin.

   Wuri ta samu ta
zauna kamar yadda kowa yake zaune a falon kafin zuwa can Abba din yace ya akayi
har hjy tazon gidan nan ace an rasa wanda zai bata abinci a cikin ku.

   Falon ya dauki
shiru ya kalli mama kafin ya juya aurin su ummah da hjy karima yace tambayan ku
nakeyi fa kun min shiru ?

    Ai gata nan a
tambayeta don ita ta saba girkawa idan tazo wake nan Abba yace wake nan fa ya
tanbayi mama din da tayi magana tace.

   Hjy salma na aika a
kawowa hjy abinci ta aiko min da maganan banza ta karasa cikin niba ruwana fa
don idan mutum yana takama da iya shege ne saimu zuba.

   Wai tsaya hjy
maimuna mu zuba din nan da kike fada
hannun ki ya rikene kin kasa zubawan ko kayan nauyi kika dauka da kika
kasa ajewa ki zuba din.

  Kai hjy maimuna kiji
tsoron Allah don raini ai kinsan cewa yau kece da girki don kawai ki hanani
kwanciyan hankali zakiyi kokarin hadani da hjy ?

   Amma kece ai kika
saba girka mata idan tazo gidan nan dama mama ta fada amma kinsan sai idan nike
da girki har in tazo gidan nan lalai ya zama wajibi na zubawa hjy girki kan .

  Kuka tsohuwar ta
saka wai an raina mata wayo ana wullakanta ta a gidan danta sai maganganu take
sakewa wanda ke nuna aibanta ummah.

    Haba haba mama
wanan maganan baikai can ba ai maganace da amsanta a zahiri ga maigirki a yau
ta kasa girka abinci ta baki ta ya wata zata dauko ta kawo maki alhalin mama a
wurinta fa kika sauka da kikazo gidan nan koda ace ba ita bace ya kamata ace ta
girka maki tunda kina side dinta hjy karima ta fada.

   Wana  naga kina son ki shige mun hanci da kudundune
a cikin gidan nan don tun zuwan ki idan zance ya taso sai kiyi kokarin dora min
laifin a kaina ?

  Eh don gaskiya
dayace a fade idan hakan ya taso haba wanan boyar Allah meye laifinta gidan nan
kan wanan abubuwan yanzu ?

    Kujeku na gode da
wanan abinda kukai min din mahaifiyata dani kun nuna min bamu da daraja a
idanun ku a, a Alh wanan zance sai idan anso a jashi amma wanan ga gaskiya a
fili kowa ya sani .

  Akan me zamu bar hjy
bamu bata abinci ba don ba wanda zai zata cewa tun shigowanta gidan nan ba a
girka mata abinci ba a gin hjy maimuna duk hjy karima ke fadan haka karshe
saita mike tsaye tana fadin Allah ya huci zuciyar ku wanan zancen maimunace mai
laifin haka ko gaba  kuliya akaje.

   Zan tafi don
wana  maganan bai shafeni ba ni yanzu
kuma naga ba a son gaskiya a cikin zancen don haka na barku lafiya hjy kiyi
hakkuri .

    Kowa ya bita da
ido don ganin yadda tasa kai ta fice daga falon ba tare da Abba ya basu umurnin
yin hakan ko nauyi yadda tayi din Abba yaji ya kira sunan ta da karima karki
sake ki kara daga kafa a wurin nan.

   Alh dole in tafi
don naga fadan rashin gaskiya kakesonyi wurin nan a yanzu  don ko gidan kuliya yana son hujja ga sharia
ai.

  Ta koma ta zauna
tana cicika saman kujeran Abba ya kallesu yace ya zama wajibi ga kowan ku daga
yanzu duk ranan da hjy tazo gidan nan kowa ya girka mata abinci a kai mata
final ku tashi ku ban wuri banson karin wani zance kuma.

    Amma mama ta fada
ya daga mata hannu yana fadin nace banson wani zance kuma ku fice min zanyi
magana da hjy.

    Hjy kiyi hakkuri
hjy karima ta fada ta fice daga falon sai ummah ta dan zaudo daga saman kujeran
da take zaune tace hjy don Allah ki yafe muna munyi kuskure hakan ba zai sake
faruwa ba itama ta fice.

   Sai mama dake
mikewa tana fadin na kula matan nan da sunana tashigo gidan nan wallahi sai
nasa tayi nadama  fadowa rayuwata a cikin
gidan nan.

   Keko kikan fara
maganan ki yanzu me kikaji ance dake kan abinda ta fada hjy tsohuwa ta fada sai
Abba ya amsa da zandai fada din hjy yanzu ina dadin irin wanan abinda maimuna
tayi ai gaskiya karima ta fada yanzu.

  Kece da girki a
dakin ki kuma hjy take zaune amma kin kasa girka mata abinda zataci don
shashanci kuma in anyi magana hjy ki tare kada a fadi.

   To ai yanzu ga yar
gaskiyan nan ta fadakar dakai gaskiyan ko da hakan wanan saurin sanyin hali
irim naka har kazo ka sake ta juyama gida daga kai har iyalin ka kuna kallo.

   Hjy wanan zancen
gaskiyane ta fada wanan itace mai laifi kuma baki son a fadi saiki tare mata to
kiyi hankali da karima  da kike gani haka
sosai don nasan da tana daga maki kafane akan komai .

   Ficewa tayi bata
tsaya jin karshem maganan shiba don bai goyi bayanta ta dau fushi dashi tana
kulla hjy karima a zuciyar ta don in batayi hankali zata iya kafa gwaunatinta a
wurin Abba don irin haka.

   Shara ya tashi
dashi yana gyaran gida da kone konen da bai samu tsayawa  yayi masu gyaran sallaba a gidan yazo kusa
don haka ysu ya tashi da gyare gyaren cikin gidan nasu.

   Yazo gurin
wanan  tumfafiyan daya fito masu a gefen
katangan gidasu din ta cikin gidan nasu mikewa yayi tsaye daga duken da yake ya
zubawa tsiron ido yana mamakin saurin girman da dan icen yayi lokaci guda.

   Wurin randan
ruwansu ya nufa ya fara debo ruwa yana zubawa icen zakace an shuka icen ne ana
son yayi girma a lokacin .

   Dijece ta fito daga
dakinta da niyar tambayanshi ya jikin nasa saidai tana  fitowan idonta yai tozali dashi a wurin
tumfafiya ya kura mai idanu kaman yana nazarin tsiron ne.

  Amadi kardai kuma
cireshi kake sonyi tanan din bayan ka barshi ya girma ya gama hayayyefa a gidan
nan koda ka cireshi a nan din indai tumfafiyace komai daren dadewa wata rana
sai ya dawo gidan nan kuma .

   Ba cireshi zanyi ba
ruwa nake zuba mashi don an dade da dauke ruwan sama baya samun ruwa murmushi
ta sake tare da fadin kaiya yaro dai yarone .

  Kai in banda abinka
Amadi kataba jin wanda yaiwa tumfafiya banruwa don ya tofu da kyawo shida keda
ruwan Allah a jikinshi ina ruwanshi da wani ruwa can.

    Ganin bai kulata
ba yaci gaba da harkokin gaban shi yasa Dije din barin wurin ta nufi wurin
murhunta don ta hura wuta ta dora masu abin kari a gidan.

   Ta gwama dan icen
daya saura masu a gidan cikin wuta na karshen take sakawa a murhun mafarkin
icen da mutumin dayazo yana mata sallama a na gobe za a fara azumi ya fado mata
a rai.

   Zubur ta dago daga
duken da take ta juyo tana kallon jikin nata dake aiki kafin ta kai kallonta
gun uwargarke dake tsaye tana kiwon ta sosai gashin jikinta ya dawo yayi kyau
yanzu.

   Ta zama cikkakiyar
akuyan data koshi da kiwo tayi bulbul da ita a yanzu kodai sai kuma ta kasa
fadan abindake kasan zuciyar nata .

   Aikin dake gabanta
ta fara bayan ta hura wuta ta dauko tukunya ta dora saman murhun ruwa ta debo
ta zuba cikin tukunyan daki ta nufa ta dauko Sauran tuwon jiya daya rage masu
gidan ta dawo ta zauna tana barewa.

   Har lokacin
mafalkin na mata yawo a zuciyarta tana kokarin tuno da abinda bakon fuskan
cikin mafalinta ya fada a ranan saidai ta kasa gin hakan .

   Bata jin zata iya
tunawa da abin saidai nan gaba kila muryan Amadine ke fadin yanzu idan mutum
yace zai tafi garin mahaifina nawa zai kashe kudin mota Dije ?

    Kaita dago tana
mashi kallon mamaki don jin abinda ya fada din a lokacin cikin mamaki ta sake
tambaysn shi Manbila fa kace Amadi ?

Leave a Reply

Back to top button