Bakar Ayah Hausa NovelHausa Novels

Bakar Ayah 8

Sponsored Links

Page 🖤08🖤

 

Hasashen sa kuwa bai tafi a banza ba,dan Hajiya zeenah tanajin an fara gangara ta mulmulawa toro ashar.
“Kai kuwa wanne ɗan rashin arziƙine,kashe mu zakayi bayan ka karbi kudi,wannan wane irin wajene na kawo kaina ni zeenatu,akan wata biyan buƙata ta duniyah. Juya juya damu na fasa zuwa garin waje saikace hanyar aljanu”
Juyowa toro yayi yana dariyah,tareda ƙarewa mutanen cikin motar kallo kafin yace.
“Ai hajiya tunda har muka ɗau hanya tofa sai munkaita casss,kuma banda abinki hawa ɗaya fah muka hau,harkin sare da tafiyar. Hm aikinci sa’a ma da ba motar ogah kika hauba,Aradu ta inaga mutuwa zakiyi muss kafin a isa,maza ma kwakwalwarsu juyewa take idan suka hau motarta zuwa gembu bareke.
Ki gode Allah ta ɗau hutu bata nan hanya bata haɗaku ba”
Duk maganar dayake Hajiya zeenah kwatakwata bata gane mai yake nufi,dan zuwa yanzu ɗankwalin ta ma yabar ƙoƙon kanta,batun gyale kam tun a hawan farko sukayi sallama.
Wani tsaunin ya nufa da mungun gudu,take kuwa su iliya suka sake zare ido tareda salati mai cikeda ihu.
A haka sukayi ta gwabzawa har zuwa wasu daƙiƙu masu yawa.
A lokacin duk wanda yaga Hajiya zeenah bazaice itace wannan matar ba mai kwalisa da kuma izzah,jikinta duk yayi dama dama da aman abincin dataci da safe,idonta yayi zuru zuru kaman wanda tayi azumin shige.
Zuwa yanxu sunyi hawa mai nisa akan tsaunin,dan sun fara shiga waje mafi duhuwa a kan wajen.
Ƙara gudun motar sukaga toro yayi tareda zurawa hanyar ido yaga ta inda wani abu zai bullo.
Aikuwa hasashensa bai tafi a banza ba,dan wasu mazane suka fito sun shafe dukkan jikinsu da da baƙin shuni,gasu murtuƙa murtuƙa,fuskar nan babu alamar rahama.
Kashe motar Toro yayi tareda waigowa ya kalli iyani,dan duk cikin motar ita kaɗaice mai ɗan dama dama a ciki,duk itama haka take kaman gawa taƙi rami.
“Keee ki kama wannan matar ki gyara,wani plan zamu haɗa,idan kuma ba haka toba tara ba har ɗari ma kunshiga a wajen wanann arnan dajin. Ni babu abinda zasu min,amma kukam bazasu ragamuku ba”
“Meyasa bazasu ragamana ba toh”
Iyani da samu damar tambayar sa cikin ƙarfin hali.
Wata soyayyar dariyah yayi kafi yasake zubamata ido wanda yasha kwalli marau.
“Iyata kenan aini da kike ganina bazasu tabani ba,saboda ni yaron BB ne,babu wanda ya isa taban a cikinsu idan na nuna musu tambarina na ƙungiyarta”
Yafaɗa yana nuna musu wani tatoo ɗin baƙar macijiya a wuyansa,an rubuta BLACK BLOOD CLUB(BB) a gefenta.
“Menene BB yake nufi kuma”
Kungiyarmu kenan,wanda shugaba take jagoranta,idan kanaso kayi tukin mambila kuma ka dunga fita lafiyah,to ka shiga kungiyar BB,muna kaiwa kudin duk wata wajenta,itakuma tana yimana shamaki da duk mai kawomana cikas daga cikin aranan jejinnan.
Suma kuma tayi yarjejeniya dasu bazasu taba yaranta ba,ita kuma zata barsu suyi nasu aikin”
“To baka ganin zasu kamamu dukka hadda kai,musamman ma idan yazamo bata nan bare ta ceceka?”
Iliya ne wanann karon ya samu damar tambayr tasa,dan bayan shugowar su cikin jejin,bayan wannan majanuniyar hanya ya kuma samun wani abin mamakin.
A yanzun ma saida toro yayi dariyah kafin yace.
“Hhhh duk yanda zan faɗamaka bazaka ganeba,duk da cewar akwai kishi kishin labarin cewar bata cikin jejinnan a yanzu,tana can kan ainihin dutse,tana rainon ɗanta data haifa wata biyu da suka wuce……duk da haka babu wanda ya isa ya taba ko dabba idan nata ne a cikin jejinnan bare kuma ku yaranta,inda badan suna tsoronta ba,mu kanmu bazasu barmu da sana’rmuba.
Amma yanxu duk wanda ya matso kusana na nuna masa tambarina amma kuma yaƙi barni,kawai dannan signal ɗin jikina zanyi,daga nan ita kuma zata ga inda duk nake…….hmmm karkuyi hasashen ma wane hukunci zasu fuskanta,saidai su tashi daga jejin gabaki ɗaya kafin tazo farautarsu”
“Tambaya biyu zanyi maka malam toro.
_shin taya zata gane sune suka tabaka to?
_sannan shin bata hanaku bayarda wanann bayanai nata mai hatsari,iyah a mota muka haɗu dakai,amma kuma harka bada wannan labarin dangane da ita,baka ganin kaima zaka iya sakata cikin matsala da wannan labarin?”
Kallon iliyah toro yayi bayan yaji mai faɗa,da wani mai shugabanne daya shiga tunanin irin bayanan daya basu,amma toro ko a jikinsa,saima ƙara kwanciya dayayi a jikin kujerar matuƙin motar.
“Amsarka ta farko,signal datake jikinmu ba guda ɗaya bace,idan mai bincike ne yakamamu da wacce zamu aika,idan aranan jejine da wanda zamu danna,idan kuma namun dajine shima da wanda zamu danna,idan kuma hatsarine shima da wanda zamu danna,in mutuwa kuma mukayi akwai wacce zata kawo da kanta.
Tambayarka da biyu kuma,bata taba cemana karmu bada bayananta ba,hasalima neman abu take wanda zata lakato wani,amma kuma babu wanda yake kulada sha’aninta,sannnan a yanda na kejin labarin ta,bata son masu mulki da masu kuɗin ƙasar nan,Sannan duk da kasancewarta jami’ar atsaro a ,yanzu kuma ko sunan bata sha’awar jinsa……..
Lahh na manta abu ɗaya ma,wani naji kace bana tsoron kukai labarinta,dan yarusulu ku kai labarinta,intaga dama ko gawarka baza’a ganiba bare kakai labari,abun ai ba yanzu aka faraba………”
Shuru motar tayi kowa yana saka labarin toron a mahangar tunaninsa,indai abinda yafaɗa da gaskene,to kuwa wannan wacece haka ,mutumce kuwa?….
Shawarar da toro yabayar suka yarda da ita,duk da saida aka tsayah hajiya zeenah ta kintsa jikinta tukunna,fuskarta kaman tayi gudawa dan rama.
Shiryawa sukayi akan Hajiya zeenah ƴar uwar mahaifiyar ta ce,saikuma iliya da iyani yaranta ne.
Cikin ɗarɗar da addu’ar Allah yasa aikinsu yayi suka fara tafiyah zuwa cikin duhuwar jejin.
Wasu irin bishiyoyine a cikin dajin masu manyan manyan ganye,da alama suna samun ruwa yanda yakamata,duhuwar da suka bayarne yabawa arnan dajin samun damar kaiwa sumame batareda matsalaba.
Lura sukayi da yanda toro yafara tafiyar da motar ta siga daban,hakanne yaƙar hauhawar gudun da zuciyarsu takeyi zuwa wani mataki mai yawa.
Signa yayi Iliya dayake gefensa tareda yimasa alamar ya suna zuwa.
Aikuwa kaman kiftawa sukaga mutane sanye da baƙaƙen kaya sun dira a gabansu,hannunsu riƙe da bindiga wasu kuma da kwari da baka.
Hailala da salati hajiya Zeenah tafara tana zazzare ido,ƙiris take jira taji ta inda za’a kawomata farmaki.
Wani daga cikinsu ne ya matso inda motartasu take,da alama shine shugabansu,dan yana sanye da jan ƙyalle maimakon baƙi kaman na sauran.
Yare suka fara shida toro,wanda su Hajiya zeenah basa jin mai suke faɗa,da alama ɗaya daga cikin yaren yankinne,bayan kaman wani lokaci ne ya juyo ya kalle su,fuskarsa da alamar mutuntawa ba kaman ɗazu ba,babu tantama Toro yasanar dashi dangan tarkasu da ogar tasa kaman yanda ya tsara.
“Hajiya ina wuni fah ya gidah?”
Yafaɗawa Hajiya zeenah cikin hausarsa da daƙyar ake ganeta.
Gyaran murya Hajiya zeenah tayi tareds tattaro dukkan jarumatarta,ta amsa masa gaisuwar batareda da sake haɗa ido dashi ba.
“Hajiya ƴaƴan ki ba irin kayanki mai kyau jikinsu,ke wane irin uwane kam?”
Zuru tayi tana kallonsa,sai yanzu da kulada kayan jikin iliyan,wata maleliyar riga ce a jikinsa,da kuma wani wandon jeans koɗaɗɗe,gwanda ma ita iyani tasaka atamfa mai fasali.
Rufe ido tayi tareda cewa
‘Iliya wataran shi zayyi ajalina da wannan shegen shigar tasa,badama a bashi kaya ko a bashi kuɗi ya siya saiya sayar ya kashe kuɗin’
Maganar toro ce ta risketa tana tsaka ta maganar zucin.
“Ka ganene,hakan ra’ayinsane,sannan kuma batare suke da hajiyan gari ɗaya ba,tafiya ce ta haɗasu yau”
Kallon rashin yarda ogan yabi toro dashi tareda cewa.
“Toro kasake rena mana hankali ne fah? Dama kayi mana wasu kwanaki fah?”
Mazewa toro yayi ganin suna son ɗagoshi tareda yin magana yana haɗe rai.
“Kaga ogah wannan ba irin na wancan bane,ni yaushe zan hanaka karbar kuɗi a wajensu,kawai dai aikin shugabane ne shiyasa,inkuma kana ganin na barka ka tabasu,sai ku ƙaƙare da ita toh”
Nazari ya tafi,yana shakkar ya kamasu kuma toro da gaske yake,yabarsu kuma toro ƙarya yake masa fah,gashi rukuninsa tunda suka fito basu kama ko ɗaya ba sai yanzu.
Haka suka cigaba da magana,babu yanda ya iya yabarsu suka wuce,dan idan yakamasu kuma toro da gaske yake to kashinsa ya bushe a wajen shigabansu,don idan BB ta tashi saita ƙwaci kusan kuɗin dasuka yi shekara suna tarawa.
Da haka su Hajiya zeenah suka tsallake tujarar mutanen dajin da taimakon toro.
Tafiyah suka cigaba dayi cikin hawa da sauƙa,zuwa lokacin babu zancen ihu ko kuma firgici,sunyi shuru sun miƙa lamarinsu ga mai duka,suna jiran sanda zasu jisu sun faɗa ko kuma toro yace musu sun iso.
Bayan gwarwarmayar da suka shiga daga ƙarshe sun kai ga isa garin gyembu shazaran majaran.
Iyani ce mai ɗan karfin hali a cikinsu,ita tasamu damar yiwa toro godiya da taimakon da yayi musu,dan har gida ta roƙeshi ya kaisu,saboda a halinda iliyah yake ciki bazai iya tuƙa motar ba
Duk abinda ake Hajiya zeenah bata sani ba,gabaɗaya hankalinta baya jikinta a lokacin.

………Toh su Hajiya zeenah tundaga yanzu anyi laushi,burin zao cika a haka kuwa?……

 

🖤 Sadi-Sakhna ce🖤
ƴar mutan jama’are

 

 

 

 

____****🖤🖤****_____

🖤 *BAƘAR AYAH* 🖤

🖤 _BOOK1_ 🖤

 

Labari/Rubutawa:SADI-SAKHNA
[ _Ƴar mutan Jama’are_ ]

 

 

 

*WATTPAD*
Https://www.wattpad.com/user/SAKHNA03

*AREWABOOKS*
https://arewabooks.com/u/sadeesakhna

______________****_______________

Leave a Reply

Back to top button