Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 49

Sponsored Links

 

SAKAYAH

 

49

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha’awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi.

Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni’ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al’ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban  lissafa. Sune manyan alamomin infection.

Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.

Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni’ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwatanta Zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.

KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni’imomin ki, da sha’awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA’AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau,  duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha’awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor’s suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.

INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi’izinillahi ta’ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma’ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya’ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 5k amman set ɗin 10k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER’N na 09097853276 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA’AURATA.

 

 

 

Cikin sauri ta girgiza kai tare da faɗin.

“A’a Nagode inada magani in mun koma zansha”.

Baki Lalla Hafsat ta taɓe kana ta fara buɗe musu Set ɗin akwatin farko na ƙasan idanunsu suka sauƙa akan wasu EGYPT Abaya masu masifar kyau da tsada baki daya cikin akwatin cike take da Abayas kala daban-daban kama daga Turkey Abaya, Itally Abaya, Dubai Abaya Wanda aƙalla zasu kai arba’in sai kuma ɗaya akwatin dake ɗauke da wasu Samfarin laffaya masu masifar kyau da tsada wanda zasu kai hamsin, sai mai binshi kuma Jakankuna da takalma masu shegen kyau da tsada sunfi set shabiyar ɗayan kuma mayafaine da mai binshi Sleeping drees masu shegen kyau da ɗaukan hankali yayinda da mai bi masa ɗan ƙaramin ke ɗauke da sarƙoƙin Gwal da ɗan kunnayensa da, kuma murjani irin na Masarautar, haka aka riƙa buɗe musu Set ɗin farko har ƙarshe ana shiga na biyun suka sake gyara zama domin ganin abin na yine, nan sukaci gaba da kallo…

 

Dai-dai lokacin kuma Moddibo suka dawo shida Ibraahim da Zakariyya suna shiga Falonsu kai tsaye bedroom Moddibo ya nufa kallonsa Ibraahim yayi tare da faɗin.

“Ya dai Yah Aleey?”.

Cikin fesar da numfashi Moddibo ya kallesa kana yace.

“So nake in ɗan watsa ruwa ne baki ɗaya yau atakure nake”.

Kai ya gyaɗa da faɗin.

“Toh ba matsala”.

 

Cike da kasala Moddibo ya nufi toilet ya watsa ruwa ya fito bayan ya fito ya shafa mai tare da feshe jikinsa da turaruka masu daɗin ƙamshi kana ya sanya Jeans Blue da Farin Riga mai guntun hannu yalwataccen sumar kansa zuwa kwantaccen sajensa yasha gyara yayin da jikinsa ke fitar da wani sihirtaccen ƙamshi.

 

Ibraahim da idanunsa ke ƙofar bedroom yace

“Wowww Yah Aleey dama haka ƙananan kaya ke masifar yi maka kyau tun da na kazo ban gaba da ƙananun kaya ba sai yau ni nai zatonma ko baka sawa ne”.

Murmushi Moddibo yayi tare da shafa sumarsa kana yace.

“Ina ɗan sawa time to time, so nake in ɗan sake dan naji yanayin garin yau kamar akwai ɗumi”.

Ya ida maganar tare da nufar kofar fita a falon yana mai ƙara matse jikinsa da Jeans ɗin da yasa don ya ɓoye yanayin da yaje ciki.

 

Zakariyya dake zaune yayi saurin cewa.

“Ya dai ina zaka je”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da buɗe su akansa kana yace.

“Zan ɗan fita ne dama ina so zan duba Asma’u”.

Ajiyar zuciya Zakariyya ya sauƙe tare da cewa.

“Ok dama ina so mu ɗanyi magana ne dan gaskiya gobe nake tunanin zan wuce amma yanzu akwai dalilin da zai tsadani”.

Anutse Moddibo ya gyara tsayuwar tare da faɗin.

“Wace magana ce?”.

Zakariyya na kallonsa yace.

“Naga kamar kuma sauri kake”.

Kai Moddibo ya girgiza tare da cewa.

“A’a In ba mai daɗewa bane ina jinka”.

Zama Zakariyya ya gyara kana ya kalli Moddibo tare da cewa.

“Toh kazo ka zauna mana”.

Baya Moddibo ya dawo kana ya zauna gefensa.

 

Numfashi Zakariyya ya fesar kana yace.

“Gaskiya nima fa naga matar Aure acikin ƙwayen Amaryanka”.

Da mamaki Moddibo ya kallesa kana yace.

“Wacce fa?”.

Hannu Zakariyya ya buɗe tare da faɗin.

“Naji dai jiya kamar ana kiranta me ma? Na dai manta sunan amma wata ƴar doguwa haka dai fara mai sanyi”.

Ahankali Moddibo yace.

“Ko dai Asiya?”.

Yatsu Zakariyya ya ƙyasta da murmushi afuskarsa yace.

“Yes of course ita, Ita nake nufi naga ta kwanta min dan tana da nutsuwa ni gaskiya yanzu bani da wani tunani in ba nata ba”.

Murmushi Moddibo yayi wanda ya sake bayyanar da kyawun fuskarsa kana yace.

“Toh Lallai dai kam toh ba laifi in Sha Allah zanyi nazari akai.

Amma yanzu bari inje idan na dawo zanyi nazari akai sai muyi maganar”.

Numfashi Zakariyya ya fesar tare da faɗin.

“Toh shikenan ba matsala amman dai ka sani ni ba irin Dr Jameel bane da zakace sai kayi nazari”.

Dariya kawai Modibbo yayi

Kana ya mike ya tafi…

 

Acan Falon su Khausar kuwa Hajja Nana ce kaɗai zaune adining area yayin da Khausar ta fito daga bedroom rabonta da abinci tun Breakfast har zuwa yanzu babu komai acikin sai tarin damun gumbuna da kuma garuka dasu tsumin masu ratsa jiki da cire yunwa da Ummi ka bata.

Sanye take cikin wani tattausan material Blue Black me ɗan ratsin Pinch daga saman rigar atsuke atake yayin daga ƙasan kuwa abuɗe yake daga ƙirjin rigan net ne haka ma hannun net ne  tayi ɗaurin ɗankwali as-down yalwataccen sumar kanta ya kwanta luf-luf bisa goshinta ,duk da cewa ba tayi makeup ba Amma tayi masifar kyau farar powder ce kawai a fuskarta sai kwalli da ta zizara aƙwayar idanunta mai haske kaman Madaran sai kuma laɓɓanta yake shiƙin Man baki sai tafi to tamkar wata tauraruwa.

 

Kallon Hajja Nana dake zaune da.

Fruits agabanta tayi cikin sanyi jiki ta nufi ɗaya daga cikin kujerun Falon zata zauna cikin tsira mata idanu Hajja Nana tace.

“Zo nan?”.

Ɗan tura baki  tayi cikin yanayin sanyin da tunda aka ɗaura aurenta ya ziyarceta tace.

“Menene?”.

Hararanta Hajja Nana tayi tare da cewa.

“Bace miki nayi kizo ba, toh kizo mana tunda na kiraki, ai in kinzo koma menene zakiji, ke da Allah yayiki ba’a miki abin arziƙi, sai yiwa mutum gardama?”.

Batare da tace Uffan ba ta nufi dining ɗin kana taja kujera ta zauna gefenta.

Cike da kulawa Hajja Nana tace.

“Meyesa bakya son cin abinci?”.

Langwaɓar da kai tayi tana wasa da yatsun hannunta, baki ɗaya tayi sanyi ahankali ta ɗago Idanunta dake ƙyallin hawaye ta kalleta.

 

Haɓa Hajja Nana ta riƙe kana tace.

“Ikon Allah kuka kuma zakiyi keda kika ce shi kike so? an kawo ki gidansa  ai sai dai kiyita dariya da farin ciki bawai kuka ba”.

Kai ta girgiza Muryanta cike da rauni ta kalli Hajja Nana tare da faɗin.

“Baza ki gane bane Hajja Nana Ina kewar Momyna sannan ina kewar Raudat, kuma yanzu gashi Haiydar ma wai ance idan antashi tafiya dashi za’a yi akace”.

Kai Hajja Nana ta jinjina kana tace.

“Eh tafiya za’a yi dashi mana, dukansu ma tafiya zasuyi nice dai zan zauna”.

Jin abinda tace yasa farin ciki ya mamaye zuciyar Khausar ahankali tace.

“Da gaske zamu zauna Hajja Nana?”.

 

Kai Hajja Nana ta gyaɗa cikin yanayinta na ƙasaita da zafi tace.

“Toh badole in zauna ba tunda kece kika ce kina son shi, bashi bane yace yana sonki, ai dole in zauna In jira inga wani irin tarba zai miki, inga kamun ludayinsa,dan wlh Allah kenan In naga ya Miki abinda bai min ba duk da ke kikace kinji kin gani kina so wallahi ɗaukarki zanyi mu tafi tare”.

Wani irin sanyayyar ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tana kallonta cike da jin daɗi dan harga Allah ta fara tsoron a tafi a barta ba kowa nata tare da mutumin da in baici zalinta ba baya jin daɗi ta kuma san baya sonta.

 

Hajja Nana kuwa cike da izzah da ƙasaita ta cigaba da cewa.

“Na faɗawa Baffanki ma tun jiya ya fara cewa inyi haƙuri kuma Wallahi babu abinda zai tafiyar dani, zama daram anan sai naga yanayin kamun ludayinsa mutumin da an bani labarin tun a makarantar ma ba shiri kuke ba kinga ko nida tafiya sai naga abinda ya turewa buzu naɗi”.

Kai Khausar ta girgiza tare da sunkuyarwa ƙasa ita kanta ta san.

Moddibo baya ko ƙaunae ganinta kuma tafi kowa sanin tsanar daya mata baya son alaƙa da ita koda kallonta ne baya son yi”.

Hannu Hajja Nana ta sanya ta ɗago haɓarta kana ta tura mata Bowl ɗin dake ɗauke da Fruits ɗin gabanta da Mukara dake ɗauke da Juice kana tace.

“Gashi kici wannan koda baki ci Abinci ba shi zai ɗan taimaka miki, kinga gaba ɗaya ki rame”

Akuma dai-dai lokacin suka ɗaga kansu suka kalli ƙofan Falon jin Antura ƙofar an shigo…

Da sauri Khausar ta sunkuyar da kanta ƙasa ganin Moddibo Hajja Nana kuwa sallamarsa ta amsa tare da zuba masa ido.

Cikin ranta tace.

“Uhmmm ai ba banza Khausar tace taji ta gani wannan kyau haka ai masha Allah, Ɗan ko maƙiyinsa yasan shi mai kyau ne”.

 

Shi kuwa Modibbo a tsakiyar Falon ya tsaya kana ya kalli Hajja Nana dake cikin shiga ta alfarma duk da tsufanta bai hanata kyawunta fita ba cikin ɗan sakin fuska  kaɗan yace.

“Ku kaɗai ne”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa masa tare da cewa.

“Eh”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Ina Innayi?”

Tana tauna Inabi ta amsa da.

“Sun sauƙa ƙasa wajen Didi”.

Ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke tare da faɗin.

“Uhmmy”.

Sai kuma ya nufi dining area ɗin.

Sassayyan numfashi Khausar ta shaƙa jin yadda ƙamshin jikinsa ya karaɗe wurin.

Shi kuwa cikin wani irin narkekken yanayi yasa hannunshi ya ɗan ja kujeran dake Facing ɗin Khausar.

A hankali ya zauna yayin da ƙamshin Kwallacar sirri da Khausar tayi amfani dashi ya cika masa hanci da ƙara sake mishi wata fitinenniyar kasala.

Kallon Hajja Nana dake shan Fruit yayi kana yace.

“Ya kike?”.

Cikin tsareshi da tace.

“Lau nake”. Da gefen idonshi ya kalleta jin yadda ta amsa kamar a faɗace, bakinshi ya ɗan taɓe tare da ɗan ƙara kwantar da kanshi jikin kujerar,

Tare da zaro wayarsa ya shiga latsawa a zahiri wayarsa yake kallon, amman a baɗinin kuwa ƙafafun Khausar dake ƙasan Table ɗin yake kallon yadda ta ɗan ɗaura ɗaya bayan ɗaya, wanda hakan ya bawa sharaɓanta dama bayyana a fili.

Khausar kuwa batare da ta ɗago ta kallesa ba ta cigaba da juya Tuffan dake hannunta batare da taci ba.

Ɗan leƙa ƙasan dining table din ya kumayi a hankali ya lunshe ido ganin tana ɗan kaɗa ƙafafunta yasashi ɗan tura nasa ƙafar dama ƙasa kusa da nata, a hankali ya zare takalminsa.

Sai kuma ya ɗan juya idonshi ya kalleta, still dai wasa take sa Apple ɗin

A hankali  ya ɗago ƙafarsa, tare ɗan mannashi kan sharabart kana a hankali ya jawoshi yayi ƙasa dashi har zuwa kan rumfar sawun nata ya shafa da sassayan tafin ƙafarshi mai taushi.

 

Da sauri ta ɗago ta kalleshi tare da sakin ajiyan zuciya dan sanyin tafin sawunshin daya ratsa mata jiki da zuciya.

Hajja Nana kuwa, baki ta ɗan sake tana kallon yadda Modibbo ya tsare Khausar ɗin da ido, sai kuma ta juya ta kalli Khausar ɗin da ta ɗan lunshe idanunta ganin shima ɗin ita yake kallo.

Jin yadda ya wani irin murza tafin kafarshi kan natane yasa ta sake buɗe idanunta tare da kallonshi tana maijin wasu baƙin abubuwan na fitowa daga cikin idanunsa suna ratsa nata idanun,

Dan shima ɗin ita ya zuwa idanunshi tamkar zai mannesu cikin nata.

Ahankali ya motsa lips ɗin sa wanda ko Hajja Nana dake gefensu bataji, abinda ya faɗa daga shi sai ita yace.

“Baki iya gaisuwa ba ko?”.

Yayi mgnar cikin kasalalelliyar muryar data sa Khausar ƙara kallonsa domin bata taɓa saninsa da wannan kuryarba.

 

Ahankali ta sake yin ƙasa da kanta tana mai ɗan jin yadda yake mata wani irin abu da yatsunsa, cikin sanyi ta kawar  da kanta gefe sai kuma ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Ina yini”.

Yana shaƙan ƙamshin Kwallacar ta dake hargitsa mushimi kwanya yace.

“Lahfeyyahhh”.

Ƙasa tayi da kanta tana cigaba da wasa da Tuffan dake hannunta ita bata gutsira ba ita bata ajiye ba sai kuma yaji gaba ɗaya jikinta na amsa sabbin yanayi sabida sautin murya yadda ya amsa mata gaisuwar da yasata jin tsikar jikinta ya bada salon yum.

Shi kuwa Modibbo a hankali ya sake sanya babban yatsansa da mai bi masa akan sangalalina zuwa kan rumfar ƙafartan yana saƙƙo dashi a hankali tare da jujjuya kan yatsar.

 

Ahankali Khausar ta ɗago manya idanunta dake sheƙi ta kallesa.

Girarsa na dama  ya ɗaga mata tare da jan dogon numfashi kana ya jingina bayansa da jikin Kujeran sai kuma ya marairaice idanunsa da suka fara rikiɗewa lokaci ɗaya wani irin yanayi ya fara ratsa sassan jikinsa musamman daya shaƙi ƙamshin Daddaɗan Kwallaca da kuma Humran da Momy ta siya mata wajen

_Aysha Aliyu Garkuwa_ .

Hajja Nana dake gefensu kuwa baki ta saki da ido cike da mamaki take binsu da kallo ganin wani irin shu’umi kana mayataccen kallon da sukewa juna kai kace tattabarune.

Da zaran ta kalli Khausar sai kuma ta juya ta kalli Namijin duniyan da shi  yama mance da ita a wurin.

 

Zamansa ya gyara tare da sake tura ƙafarsa ya taɓa ƙafanta da kyau.

Ahankali ta kuma ɗaga manyan idanunta ta kallesa.

Ganin tana kallonsa yasa ya mata Signal tare da kashe mata ido ɗaya.

 

Ya Salam shine abinda ta iya faɗi cikin ranta.

Sabida abin yazo mata da saƙonni masu zafi, shi Modibbo ne kuwa, ya akayi haka harda signal abun yan ikkah ya iya.

 

Shi kuwa Modibbo cikin wani irin amintaccen yanayi ya kuma ɗaga mata girarsa ɗaya, sai kuma ya miƙe daga jinginar da yayi daga jikin Kujeran ya zauna dai-dai. Cikin yanayin gaza sarrafa tunaninsa da jikinsa ya ɗan fesar da numfashi tare da laso lips enshi kana a

hankali ya ɗago hannunsa tare da kafa guiwar hannun nasa, bisa table ɗin.

Hannunta dake kan Mug din dake gabanta  ya riƙo cikin nasa hannun.

A tare suka ja nannauyan numfashi, kana a tare suka fesar da numfashin.

Ita kuwa Khausar ɗaya hannun nata  da har zuwa lokacin take riƙe da Apple taci gaba da jujjuyawa tana maijin tamkar saman gajumare yake turata.

Yayinda shi kuma  gwiwar hannunsa ke tokare da table ɗin.

Cikin yanayin mamaki ta buɗe Idanunta da baki tana kallonsa.

Gira ɗaya ya sake ɗaga mata yana lumshe idanunsa, a hankali ya matse hannunta  acikin nasa bawai yanda zataji zafi irin dai ƴar matsarnan da tafi kama da tausaya yayiwa hannun yatsunta ya ɗan matse tare da zubawa faratunta ido .

 

Cikin wata irin kasala mai cike da shauƙi da dawowar yanayin da ya rayu kafin a sace J ɗinsa ya dawo mishi sabo,  motsa laɓɓansa yayi a hankali tare da sanya ƙwayar idanunsa anata kana yace.

“Yahh mukayeeh dahh kehhh?”.

A kasalance ta lumshe idanunta acikin nasa kana ta buɗesu, baki ɗaya yanayin da yake mata magana ya tsumata wani irin yanayi take ji yana huda ko wani magudanan jinin jikinta yayin da sautin muryansa ke ratsa har ƙoƙon zuciyarta cikin wata shagwaɓaɓbiyar murya ta kalli idanunsa kana ahankali ta furta.

“Akan me ɗin?”.

Da sauri ya matse jikinsa, kana ya lumshe idanunsa sautin Muryanta nayi masa amsa kuwwa acikin dodon kunnensa yace.

“Ba cewa nayi ki yanke farcen nan ba?”.

Langwaɓar da kai tayi tana lumshe idanunta ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Zan yanke ai”.

Numfashi ya fesar kana yace.

“Sai yaushe kenan?”.

Shiru tayi ta gaza cewa komai, sai zubawa sajensa ido da tayi sabida salonshi ya fara a yanayin da bata zataba.

Shi kuwa cikin sanyi ya ɗan ƙara matsowa tare yin mgnar can ƙasan maƙoshi yace.

“Ba tun jiya nace ki yanke ba baki yankeba, still yau ɗin tunda gari ya waye baki yanke ba har yanzu”.

 

Ta wani langwaɓar da kai tana mai narkar da ƙwayar idanunta cikin nasa tare da faɗin.

“To ai zan yanke”.

Baki sake Hajja Nana ke kallonsu ta kalli Khausar ta kalli Moddibo dake riƙe da hannun Khausar yana shafa saman tafin hannuntan da babbar yatsarshi ga wani irin fitinennen kalo da yake binta dashi kai kace zai cinyeta ɗanye ita kuwa Khausar duk ta saki da alamun da zata samu dama narkewa zatayi a jikinshi.

 

Moddibo kuwa har ga Allah har cikin ransa ya manta da cewa akwai wani mutum awajen.

Cikin lumshe idanu ya cigaba da shafa ƙafanta Khausar kuwa wani irin yanayi take ji aduk lokacin da sanyayyar yatsunsa suka sauka akan sharaɓanta.

Hajja Nana kam ta gaza ɗauke idanunta akansa kallon ikon Allah kawai take.

 

Ita kam Khausar jin yanda yatsun ƙafansa ke yawa anata yasa cikin kasala tace.

“To ai zan yanke”.

Kai ya girgiza still Muryansa ƙasa-ƙasa yace.

“Um-um baza ki yanke ɗin ba”.

Da sauri ta ɗan ware idanunta acikin nasa dake cike da zallan fitina da mayata tace.

“Allah zan yanke”.

Sassayan numfashi ya  fesar tare da faɗin.

“Ko dai kinfi so ni ɗin na yanke mikinne?”.

Da ɗan sauri ta girgiza masa kai tunawa da tayi jiya cewa yayi idan zai yanke zai haɗa da kan ƴan ya tsunta.

Hajja Nana kam sai raba ido take ta kallesa ta kuma kalli Khausar kallon ikon Allah da abin al’ajabi take aranta tace.

“Iyye kaji ƴaƴan zamani kaji ja’irin yaro agaban nawa lahaula fisha’atillahi”.

Moddibo kam har ga Allah ya manta da ita awajen.

Yayin da Khausar ma halin da Moddibo ya jafeta na wani irin kasala da mutuwar jiki yasa ta mance da ita Allah yasani da zata samu kwanciya takesonyi sabida jikinta daya gama sakewa tuno nitsuwa da salaman da taji lokacin daya ruggume ta yasa takejin da jikinshi da tayi bacci.

 

Cikin nutsuwarsa da kuma yanayin da yake ciki ya ɗan fusgo hannunta dake cikin nasa wanda yasa dole Khausar matsowa ya zamana ɗaya hannunta ya sauƙa akan table ɗin ga mamakinta sai taji ya kai ƙaramin yatsarta cikin bakinsa.

 

Yana kai ya tsanta cikin bakinsa Hajja Nana ta rumtse idanunta da ƙarfi tare miƙewa da sauri tabar wajen jikinta na rawa, ganin rashin kunyar da suke ba abinda take maimaitawa abakinta sai Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un gani take kamar saɓon Allah suke, wannan wace irin fitina da tsaurin ido ne da yaran zamani sukeyi, yaro salla-salla ashe ashe ko al’wala bai iyaba ita kuma hegiya kamar ba ita ke kuka yanzu, sai wani lumshe ido take kamar ɓera na lasar gari wato ita hegiya ga miji ko, Allah mai iko. har ta fice daga wajen tana jajanta al’amarin aranta tana mgnar zuci.

 

Moddibo kuwa yana sa yatsarta abaki ahankali ya manna yatsar tsakiyar harshensa.

A tare suka lumshe ido domin kusan a tare baƙon lamarin ya ziyarcesu.

Kusa 1 minute sukayi a haka kana suka buɗe idon a tare.

Manyan idanunsa da suka sirance ya liƙa mata, kana ya fara ɗan datsa dai-dai kan farcen da haƙoransa na gaba, ahankali yake cigaba da datsawa yana mai lumshe idanunsa har ya gama cire farcen.

ahankali ya zare yatsan daga bakinsa, kana ya ɗan kawar da kansa gefe tare da tufar da farcen.

Idanunsa da suka sake rikiɗewa ya mayar kanta kana ya ɗaga mata girarsa.

Khausar kuwa kallon ƙwayar idanunsa take tana hango wani fitinan nan al’amari acikinsu wanda ya sake haddasa mata kasala da wani irin baƙon al’amari Narkewa take tamkar kitsen ji take tamkar bazata iya sarrafa kanta azaune ba.

 

A hankali ya kuma maida yatsan baki ganin kamar farcen bai gama yankuwa ba cikin kasala ya datse shi kana ya tofar wani irin tsuma naman jikinsa keyi daga can ciki.

Sai kuma ya sake kamo  mai binsa shima ya sanya abakinsa ya datse.

Idanunta dake lumshe ta buɗe jin hannunsa dake riƙe da nata yana kar-karwa ta ɗan kallesa.

Shima kallonta yayi kafin ahankali yayi wani irin miƙa kana ya maida ƙaramin yatsanta bakinsa wanda ya yanke cikin wani irin salo da tsananin shauƙi ya shiga tsotsan ya tsan tamkar wanda ya kama Fida.

Atake taji tsikan jikinta ya miƙe yam-yam wani irin abu taji yana ratsata tun daga tsakiyan kanta har tafin ƙafanta.

Da sauri ta lumshe idanunta.

Cikin wani irin yanayi da bai taɓa riskansa ba ya buɗe Idanunsa ya kalli yanda ta runtse nata da kuma yanda jikinta ke tsuma da kuma yanayin fitinennen lasala daya bayyana tare da ita.

Ahankali ya zare tsayan tare da fitarwa daga bakinsa jin ya fitar da yatsan yasa ta buɗe Idanunta ta kallesa jin yanda baki ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa ga kuma ƙwayar idanunsa da suka cika taf da hawaye.

Ahankali ya lumshe Idanunsa sai ga hawaye sharrr sun z….

 

 

*Masu son Maganin infection da maganin mata, ku marmatso wannan account no in ne naku ta ciki zaku turo kuɗin ku 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, Sai ki turo shaidar biyanki ta WHATSAPP NUMBER’N na 09097853276. akwai sabbin kaya masu zafi suna nan bisa hanya, ki turo kuɗinki a saki cikin lissafi. Kayanen mata masu zafi sadidan daga Chadi akwaisu Garukan daka, gumbunan, Tsumummuka, cida Ciccibi Abodi cida kaza ci da jan nama kwanon ƙasaitacciyar mace biyar sirri, furar mata, gumbar madara Gumbar kolli mai ƙyallin al’khairi gumbar uku al’khairi, gumbar da ba’a baiwa mai kishiya, gumbar riɗi, garin maɗi garin melɗamhi garin ilanwaddihi garin mallaka, tsumin riɗi tsumin tsirtai tsumin kinfi budurwa, tsumin riɗi, tsumin ta baje Sabaya, matsin maliƙi mai masifar matse mace matsin daɗi har maɗiga, mai ɗan kare kyau. Kullacar sirri al’ajabu shu’umar Humra, da duk sauran kan ƙamshi. Haɗin amarya budurwa ko bazawara haɗin mai jego ko uwar gida, akwaisu Available set ɗinmu hawa hawane akwai manya akwai ƙananan, ƙanan daga 40k ne 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙarami haɗina na karshe sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar shi 7k ne shine ƙarshen haɗina kenan… Manyan set ɗin kuma daga 50k 60k 70k 80k 90k 100k ke zaki faɗi haɗin nawa kikeso anyi miki kana kimin bayanin yadda kikeso da matsalarki ni kuwa nasan abinda zan haɗa miki, ina araha kam amman ina hana bashi*

 

 

 

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button